1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana faragabar sake bayyanar Ebola a Saliyo

Gazali Abdou TasawaJanuary 15, 2016

Kasar Saliyo ta ba da sanarwar a jiya Alhamis soma gudanar da bincike kan mutuwar wani dan kasar tata da ya rasu a wani gidan assibiti na kasar da kuma binciken farko ya nunar da cewar cutar Ebola ce ta kashe shi .

https://p.dw.com/p/1He0d
Sierra Leone Regierung bestätigt Todesfall durch Ebola
Hoto: Getty Images/AFP/F. Leong

Kasar Saliyo ta sanar a jiya Alhamis da soma gudanar da bincike kan mutuwar wani mutun dan kasar tata da ya rasu a wani gidan assibiti na garin Magburaka na cikin karamar hukumar Tonkolili a Arewacin kasar da kuma ake kyatata zaton cutar Ebola ce ta kashe shi .

Wani jami'in ofishin ministan kiwon lafiya na kasar ta Saliyo ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa wani binciken farko da suka gudanar a kan gawar mutuman a jiya Alhamis ya nunar da cewa Ebolar ce ta kashe shi. Amma kuma za su kara gudanar da karin wani binciken wanda ake sa ran bayyana sakamakonsa a wannan Jumma'a.Wannan warwarewar asalati ta zo ne kwanaki kalilan bayan da Hukumar lafiya ta Duniya WHO ko OMS ta bayyana kawo karshen cutar ta Ebola a kasar Laberiya dama illahirin kasashen yankin da suka yi fama da cutar a tsawon shekaru biyu.