1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana iya soke taimakon EU ga Falasdinawa idan Hamas ta lashe zabe

December 18, 2005
https://p.dw.com/p/BvFv

Babban jami´in kula da harkokin ketare na KTT Javier Solana ya ce idan kungiyar Hamas ta yi nasara a zaben da za´a gudanar a yankunan Falasdinawa a watan gobe kuma ta ki yin watsi da tashe-tashen hankula, to kungiyar EU ka iya daina ba wa hukumar mulkin Falasdinu duk wani taimako. Kungiyar Hamas ta Falasdinawa masu gwagwarmaya da makami, na da hannu a jerin hare haren kunar bakin waken da ake kaiwa Isra´ila wadanda kuma suka yi sanadiyar mutuwar daruruwan Yahudawa. Kungiyar ta lashe mazabu da dama a zabukan kananan hukumomi da aka gudanar cikin makon jiya a Gabar Yammacin Kogin Jordan. Hamas ta tsayar da ´yan takaran a zaben majalisar dokokin da zai gudana a ranar 25 ga watan janeru mai zuwa. An kiyasce cewar taimakon da EU zata ba Falasdinawa a shekara ta 2006 ya kai euro miliyan 260.