1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana shirin yin tattaunawa tsakanin Ahmedinejad da sarki Abdullah na Saudiya

March 3, 2007
https://p.dw.com/p/BuQh

Shugaban Iran Mahmud Ahmedi Nijad ya ce zai yi amfani da ziyararsa ta biyu a Saudiya don tattaunawa akan yadda Iran da daular ta Saudiya zasu iya aiki tare don rage hauhawar tsamari a yankin GTT. Shugaba Ahmedi Nijad ya fadawa manema labarai a filin jirgin saman birnin Teheran kafin ya tashi zuwa birnin Riyadh cewa zai tattauna da sarki Abdullah akan hadin kan da za´a bawa juna a cikin duniyar musulmi da kuma yankin GTT. Shugaban na Iran wanda Amirka ke zargin kasarsa da dagula lamura a yankin, ya ce a shirye Iran ta ke ta yi duk iya kokarin ta don rage rigingimun siyasa a Lebanon. A yau dai ne Ahmedi Nijad ke fara ziyarar aiki ta yini biyu a Saudiyya, wadda take zama babbar kawar Amirka.