1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugabar gwamnatin Jamus za ta kai ziyara Faransa

Suleiman BabayoNovember 20, 2015

Ziyarar shugabar gwamnatin Jamus tana zuwa ne yayin da aka cafke wani dan gudun hijira a Jamus bisa masaniya a kan abin da ya faru a Paris.

https://p.dw.com/p/1H9n9
Deutschland Merkel Rede beim 9. Nationaler IT-Gipfel in Berlin
Hoto: picture-alliance/dpa/W. Kumm

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta bayyana shirin kai ziyara birnin Paris fadar gwamnatin kasar Faransa domin tattauna hanyoyin hadin kai bisa yaki da ta'addanci. Ofishin jakadancin kasar ya ce ranar Laraba mai zuwa Merkel za ta kai wannan ziyara.

Haka yana zuwa yayin da masu bincike na Jamus suka kama wani dan gudun hijira daga kasar Aljeriya, wanda ake zargi yana da masani kan hare-haren birnin Paris tun lokacin da ake kitsawa, kuma ya yi biris wajen shaida wa hukumomi. An kama dan gudun hijiran a garin Arnberg na Jihar Nord Rhine-Wesphalia. Kasar ta Jamus tana nuna yuwuwar samun 'yan gudun hijira fiye da 900,000 cikin wannan shekara.