1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Desmond Tutu ya koma gida

Yusuf BalaJuly 21, 2015

Dan tahaliki da ya samu lambar yabo ta zaman lafiya a duniya, na da shekaru 83 ne sannan an maida shi asinbiti ne a makon da ya gabata bayan harbuwa da wasu kwayoyin cuta.

https://p.dw.com/p/1G2Eu
Deutschland Desmond Tutu in Lübeck
Desmond Tutu malamin majami'a dan fafutikaHoto: picture-alliance/dpa/D. Reinhardt

Wata kungiyar agaji da jinkai da kare hakkin bil'Adama a kasar Afirka ta Kudu ta bayyana cewa babban malamin majami'ar nan archbishop Desmond Tutu ya koma gida bayan mako guda a asibiti bisa umarnin likita da ya nemi ya zauna ya huta. A jawabin da cibiyar Desmond and Leah Tutu ta fitar, ya nunar da cewa babban malamin majami'ar ya koma gida ne a ranar Talatan nan.

Iyalan archibishop Tutu sun bayyana godiyarsu ga likitoci da ma sauran jama'a saboda nuna musu kauna da suke yi.Dan tahaliki da ya samu lambar yabo ta zaman lafiya a duniya, na da shekaru 83 ne sannan an maida shi asinbiti ne a makon da ya gabata bayan harbuwa da wasu kwayoyin cuta amma ya samu sauki bayan ya sha magunguna nau'in antibiotics.

A cewar 'yarsa Mpho Tutu rashin lafiyar da mahaifinta ya samu aka kai shi asibiti a wannan lokaci ba ta da alaka da ciwon da yake fama da shi na daji da kan kama maraina, shekaru 18 kenan da ya samu cutar.