1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Aski ya kai gaban goshi kan ficewar Birtaniya daga EU

Mohammad Nasiru Awal
March 21, 2017

A karshen watan Afrilu kungiyar EU za ta yi taron koli na musamman kan ficewar Birtaniya daga tarayyar Turai.

https://p.dw.com/p/2Zdbr
Polen Donald Tusk
Donald Tusk shugaban majalisar zartaswar tarayyar TuraiHoto: picture alliance/dpa/A. Vitvitsky/Sputnik

Shugaban majalisar zartaswar kungiyar tarayyar Turai EU, Donald Tusk ya sanar a wannan Talatar cewa zai kira wani taron kolin membobi 27 na kungiyar ba tare da Birtaniyya ba a ranar 29 ga watan Afrilu, inda za a tattauna game da ficewar Birtaniya daga EU. Tusk ya ce abinda za a ba wa fifiko shi ne samun tabbaci da kuma fayyace wa dukkan al'ummomin Turai da kamfanoni da kuma kasashe membobi wadanda ficewar Birtaniyar za ta shafa.

Ya ce: "A dangane da sanarwar da aka bayar ranar Litinin a birnin London, ina mai shaida muku cewa zan kira wani taron kolin kungiyar EU a ranar 29 ga watan Afrilu inda za mu amince da ka'idojin tattaunawar ficewar Birtaniya. Da na so a ce Birtaniya ba ta zabi ficewa daga EU ba, amma mafi rinjayen masu zabe a Birtaniya sun yanke hukunci na daban. Saboda haka za mu yi kokarin ganin illar da shirin rabuwar zai janyo kadan ce."

A ranar 29 ga watan nan na Maris Birtaniya za ta fara shirye-shiryen rabuwa da kungiyar EU, inda za a kaddamar da tattaunawa ta tsawon shekaru biyu tsakanin bangarorin biyu.