1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Barazanar ɓarkewar saban rikici a Sudan

Sadissou YahouzaOctober 10, 2010

Shugaba Omar Hasan Al -Bashir na Sudan ya bayyana barazanar ɓarkewar saban faɗa tsakanin yankunan kudu da arewancin ƙasar.

https://p.dw.com/p/PaQ7
Omar Al-Bashir da Salva KiirHoto: picture-alliance/dpa/dpaweb

A yayin da ya rage watani uku kacal a shirya zaɓen raba gardama na neman yancin kan yankin kudancin Sudan, alamu na ƙara nuna sake abkuwar wani saban faɗa tsakanin gwamnatin Sudan da tsafin´yan tawayen SPLM.

A wani jawabi a ya gabatar jiya birnin Syrthe na ƙasar Libiya shugaban ƙasar Sudan Omar Hasan Al Bashir ya zargi SPLM da yin fatali da wasu daga ƙa´idodin yarjejeniyar zaman lafiya da su ka rattaba wa hanu a shekara 2005.

Jawabin na shugaba Albashir ya bayyana buƙatar sake saban zama, domin tattana wannan matsaloli, matakinda yankin kudancin Sudan ya yi watsi da shi. 

A wannan mako Komitin Sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya ya tura tawaga ta mussamman a yankin Kudancin Sudan domin gani da ido inda aka kwana game da shirye-shiryen wannan zaɓe.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi

Edita: Ahmed Tijani Lawal