Barazanar kai harin ta'addanci a Jamus
November 21, 2010Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta tabbatarwa da al'ummar ƙasar cewar, gwamnati ta ƙara ƙarfafa matakanta na tsaro domin kare lafiyarsu daga barazanar ta'addanci.
"Muna fuskantar mummunan barazanar 'yan tarzoma, wanda ake gani a zahiri, kuma an jima ana magana akai. Amma ba za mu taɓa durƙusar da walwalar jama'a ba, ta irin wannan barazana. Dangane da haka ne muka ƙara matakan tsaro a dukkan sassan ƙasarmu. Jama'a na iya cigaba da gudanar da harkokin rayuwarsu na yau da kullum ba tare da wata fargaba ba."
Tun daga ranar Laraba ne dai ministan harkokin cikin gida na Tarayyar Jamus ya faɗaɗa matakan tsaro, bayan ya sanar da barazanar kai hari, duk da cewar babu cikkaken bayani.
Mujallar Der Spiegel ta Jamus ɗin dai ta ruwaito cewar, akwai yiwuwar kaiwa ginin majalisar ƙasar ta Reichstag da ke birnin Berlin hari, a farkon shekara mai kamawa.
Mawallafiya: Zainab Mohammed Abubakar
Edita : Mohammad Nasir Awal