1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Birtaniya ta bukaci taimakon EU

February 17, 2018

Firaministar Birtaniya Theresa May, ta bukaci hadin kan kungiyar Tarayyar Turai EU ta fuskar mu'amalar tsaro bayan ta fice daga cikin kungiyar.

https://p.dw.com/p/2srH7
München MSC 2018 | britische Ministerpräsidentin Theresa May
Hoto: Reuters/R. Orlowski

Firaministar Birtaniya Theresa May, ta bukaci hadin kan kungiyar Tarayyar Turai EU ta fuskar mu'amalar tsaro bayan ta fice daga cikin kungiyar. Yayin jawabin da ta gabatar lokacin taron harkokin tsaro a birnin Munich, madam May ta ce rayuwar jama'a na cikin hadari.

Ta amince cewa babu wata kasa ta daban da ta fi Birtaniyar kyawun alaka da kungiyar ta EU, a saboda haka ne take cewa babu dalilin da zai hana su cimma wannan bukata. Firaministar ta Birtaniya, ta kuma ce ba za su bata lokaci wajen cimma batun na tsaro ba, tana mai gargadin kasashen Turai da su guji sanya siyasa cikin matsalolin da suka shafi kokari na yaki da ta'addanci.