1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta afkawa wani kauye

Ahmed Salisu
August 13, 2017

Labarin da muke samu daga Najeriya na cewar 'yan kungiyar nan ta Boko Haram sun hallaka mutane hudu tare da kone gidaje da dama a kauyen Amarwa da ke da tazarar kilomita 20 da birnin Maiduguri fadar jihar Borno.

https://p.dw.com/p/2i9jA
Bisheriger Anführer der nigerianischen Miliz Boko Haram Abubakar Shekau
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Masu aiko da rahotanni suka ce 'yan Boko Haram din sun shiga kauyen ne da misalin karfe 11 na daren jiya Asabar idan suka kama yin harbi irin na kan mai uwa da wabi kafin daga bisani kuma suka fara cinnawa gidajen mutane wuta. Wani basaraken a garin ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewar biyu daga cikin wanda aka kashe sun rasu ne sakamakon harbin bindiga yayin da saura biyu suka rasu a wasu daga cikin gidajen da aka kone. A watan Mayun da ya gabata ma dai wannan kauye na Amarwa ya fuskanci harin 'yan Boko Haram wanda suka yi wa kauyen tsinke a kan babura kana suka harbe wasu manoma shidda har lahira a lokacin da suke yin shuka.