1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta halaka rayuka a Najeriya

Ramatu Garba Baba
August 25, 2017

Wani harin kwanton bauna na tsagerun kungiyar Boko Haram masu dauke da makamai ya janyo mutuwar mutane biyar a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

https://p.dw.com/p/2iqAh
Nigeria Aufarbeitung Terrorismus Boko Haram Straßensperren
Hoto: DW/K. Gänsler

An tabbatar da mutuwar mutane biyar a harin kwanton bauna da ake zargin mayakan kungiyar Boko Harama da kai wa a  jahar Borno da ke a arewa maso gabashin kasar, an kai harin ne a wannan Alhamis akan ayarin motocin sojoji da ke samun rakiyar jami'an sa-kai na kato da gora a kauyen Meleri na karamar hukumar Konduga, mayakan sa kan hudu da direban motar guda ne suka rasa rayukansu a cewar shugaban 'yan kato da gora na wannan yankin.