1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta kai hari a Kamaru

Ramatu Garba Baba
August 25, 2017

Hukumomi a Jamhuriyar Kamaru sun ce mayakan Boko Haram sun halaka mutane 11 tare da yin garkuwa da wasu 8 a yankin arewacin kasar.

https://p.dw.com/p/2irsY
Kamerun Selbstmordattentat in Kolofate
Hoto: Getty Images/AFP/Stringer

Mayakan na Boko Haram sun kaddamar da harin ne a cikin daren da ya gabata a kauyen Gakara da ke a kan iyakar Kamarun da Najeriya, bayanai daga bakin mazauna yankin da lamarin ya faru na cewa maharan sun kona gidaje kimanin 30 a wannan harin.

Majiya daga ma'aikatar tsaron kasar na cewa mayakan da ake zargi 'yan  kungiyar Boko Haram ne sun halaka mutane goma sha daya a harin tare da yin garkuwa da wasu mutane takwas harin da suka kai a yankin arewacin kasar.