1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram za ta sako 'yan matan Chibok 83

October 16, 2016

Fadar shugaban Najeriya ta ce kungiyar Boko Haram ta amince ta saki 83 daga cikin 'yan matan nan Chibok da suka sace shekaru biyun da suka gabata bayan da a 'yan kwanakin da suka gabata suka saki 'yan mata 21.

https://p.dw.com/p/2RHx0
Screenshot mutmaßliches Boko Haram Video
Hoto: youtube/Fgghhfc Ffhjjj

Garba Shehu da ke magana da yawun shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce bangaren kungiyar da ke rike da 'yan matan ya bayyana cewar a shirye ya ke ya saki 'yan matan in har za a zauna kan teburin tattaunawa da shi. Kakakin na gwamnatin Najeriya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewar shi wannan bangare wanda Musab al-Barnawi ke shugabanta ya ce sauran 'yan matan na hannun daya bangaren kungiyar ta Boko Haram wanda Abubakar Shekau ke jagoranta.