1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shekaru 71 da da harin Amirka a Japan

Gazali Abdou TasawaAugust 15, 2016

Kasar Japan na gudanar da taron tunawa da zagayowar ranar cikar shekaru 71 da yin sarandar da ta kawo karshen yakin yankin Pacipic, na lokacin yakin duniya na biyu.

https://p.dw.com/p/1JiJl
Japan Tokio Yasukuni Schrein Gedenken Kriegsende Rechtsaktivisten
Hoto: Reuters/K. Kyung-Hoon

A ranar 15 ga watan Agustan shekara ta 1945 ne dai Amirka ta kai wasu tagwayen hare-haren nukiliya a biranen Hiroshima da Nagasaki na kasar ta Japan, sarkin kasar na wancan lokaci Hirohito ya fito ya yi jawabin mika wuya kasarsa a wannan yaki. Da ya ke jawabi a gurin taron tunawa da wannan rana, Sarki Akihito mai shekaru 82 a duniya wanda kuma da ne ga tsohon sarkin marigayi Hirohito, ya bayyana cewa yana takaici idan ya waiwayi tarihin abin da ya wakana a baya, inda ya ce yana fatan yaki irin wannan ba zai kara afkuwa a nan gaba ba. Mutane sama da miliya uku ne dai da suka hadar da sojoji da fararen hula a kasar ta Japan, suka rasa rayukansu a yayin yakin duniyar na biyu.