1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

China za ta samar da tashar Nukiliya a Sudan

Kamaluddeen SaniMay 24, 2016

Hukumomin birnin Khartoum na Sudan a yau sun bayyana cewar wani kamfanin kasar Sin ya sanya hannu kan wata yarjejeniyar samar da tashar Nukiliya a kasar ta Sudan da ke zama irin sa na farko.

https://p.dw.com/p/1ItfV
Omar al-Baschir ARCHIV
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Elmehedwi

Kamfanin harkokin Nukiliyar Sin mai suna CNNC ya sanya hannu kan yarjejeniyar da ma'aikatar samar da hasken wutar lantarki ne a jiya litinin domin samar da tashar da zata taimakawa kasar wajen samun hasken wutar lantarki.

Yarjejeniyar ata cewar mai magana da yawun ma'aikatar lantarkin Mohammed Abdelrahim zata tallafawa kasar a nan gaba domin bunkasa harkokin samar da makamashi don amfanin al'ummar kasar.

Yanzu haka dai Sudan din tana da karfin mega watt dubu uku a yayin da ke matukar bukatar samun karin megawatts nan da shekaru masu zuwa.