Ci gaban ɓarin wuta a Somalia
April 24, 2007Talla
A ƙasar Somalia, ana ci gaba da ɓarin wuta tsakanin dakarun gwamnati, masu goyan bayan Ethiopia, da kuma na kotunan Islama.
Yau kwana na 7 kenan, da ɓangarorin 2 ke gwabzawa, da manyan makamai.
Gwamnatin ta alƙawarta cewar dakarun ta za su ci gaba da fafatawa, har sai sun kakkaɓe yan yaƙin sunƙuru daga ƙasar Somalia.
A cewar ƙungiyoyin masu zaman kan su, ya zuwa yanzu, a ƙalla mutane 30 su ka rasa rayuka, a tsukin kwanaki 7 da su ka gabata.
Sannan kussan mutane rabi milion su ka shiga halin gudun jihira.
A sahiyar yau, faɗan ya ƙara tsamari, bayan da sojojin gwamnati, su ka yi luggudan wuta, ga yankunan yan yaƙin sunƙurun.
Wannan shine bala´i mafi muni, da ƙasar Somalia tun bayan kiffar da shugaba Mohamed Siad Bare, a shekara ta 1991.