1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ci gaban rarrabuwar kawuna a cikin jam'iyyar MPN a Nijar

December 28, 2016

Bayan Jihar Maradi sauran wakilan jam'iyyar na MPN kishin kasa sun gudanar da wani taro a Tahoua domin yin kashedi ga shugban jam'iyyar Ibrahim Yacouba.

https://p.dw.com/p/2Uxpt
Ibrahim Yacouba shugaban jam'iyyar MPN kishin kasa
Ibrahim Yacouba shugaban jam'iyyar MPN kishin kasaHoto: I. Sanogo/AFP/Getty Images

A Jamhuriyar Nijar, wani takon sako ne ya kuno kai a cikin  jam'iyyar MPNKishin kasa inda 'ya'yan jam'iyyar ke zargin jagoran na su da kula rarrabuwar kawunan magoya bayan jam'iyyar tare da nuna mallakar jam'iyyar, abin da ya janyo wasu ya'yan jam'iyyar suka gudanar da taro domin yin kshedi ga shugaban jam'iyyar.Tun da farko dai an samu irin wannan rikici a cikin jam'iyyar a Jhar Maradi inda aka girka sabon shugaban jam'iyyar na jihar abin da ya janyo rashin yardar wani bangaran jam'iyyar.