1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ci gaban rikicin Somalia

June 15, 2007
https://p.dw.com/p/BuIi

A ƙalla mutane 8 su ka rasa rayuka a ƙasar Somalia, a cikin wasu tagwayen hare-hare, da su ka rusta da birnin Mogadiscio.

Hare-haren sun yi setin mataimakin magajin garin Mogadiscio Osman Dagatur, wanda ya ƙetara rijiya da baya.

Gwamnati ta rataya alhakin wannan hari, ga dakarun kotunan Islama.

Tun bayan korar kotunan Islama,daga karagar mulkin Mogadiscio, babban birnin na Somalia, ke fama da tashe-tashen hankulla.

Masu tsatsauran ra´ayin addinin Islama, sun sha alwashin ɗaukar fansa, da kuma cilastawa sojojin Ethiopia, da su ka kawo tallafi ga gwamnati, su fice daga ƙasar Somalia.