1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ci gaban yaƙi a Libanon.

June 8, 2007
https://p.dw.com/p/BuJX

A ƙasar Libanon a na ci gaba da ɓarin wuta, tsakanin dakarun gwamnati, da ƙungiyar Palestinawa yan gudun hijira ta Fatah Al-Islam.

Ya zuwa yanzu, a na fuskantar rikici mafi tsanani, a matsungunan yan gudun hijira, na yankin Nahr Al Bared , amma ƙungiyar ta yi barazanar bazuwar yaƙin a wasu sassan Libanon, muddun rundunar gwamnati, bata dakatar da ruwan harsasai ga yankin ba.

Manyan mallumai masu faɗa aji a yankin, sun yi tayin shiga tsakani, ba tare da cimma buri ba.

Gwamnatin Libanon ta alƙawarta ci gaba da farautar yan takifen, har sai sun yi saranda.

A nata ɓangare, ƙasar Amurika, ta ƙara aika tallafi makami, domin karfafa gwiwar ƙasar Libanon, ta yaƙi al´ammuran ta´adanci.