1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Da alamu an kusa warware rikicin lardin Darfur dake yammacin Sudan

May 12, 2006
https://p.dw.com/p/Buyh
Bisa ga dukkan alamu gwamnatin Sudan zata mika kai ga bukatun kungiyoyin ´yan tawayen nan biyu, wadanda suka ki sanya hannu kan yarjejeniyar wanzar da zaman lafiyar yankin Darfur a makon jiya. Shugaban babbar kungiyar ´yan tawaye ta Sudanese Liberation Army, Abdel Waheed Mohammed al-Nur ya ce ya samu wata amsa mai karfafa guiwa daga gwamnatin Khartoum a dangane da shawarwarin da ya bayar a ranar laraba, wadda ta nemi gwamnati ta biya diyya mai yawa ga al´uman yankin na Darfur. A cikin makon jiya aka sanya hannu kan yarjejeniyar a birnin Abujan Nijeriya tsakanin gwamnatin Sudan da babbar kungiyar ´yan tawayen Darfur, da nufin kawo karshen yakin da aka shafe shekaru 3 ana yi a wannan yanki.