1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wani rahoto ya ce dakarun Faransa na wani yakin boye a Libya

Mohammad Nasiru AwalFebruary 24, 2016

Jaridar Le Monde da ta buga wannan labari ta ce Faransa na wani yaki a boye da kungiyar IS mai ikirarin jihadi a Libya.

https://p.dw.com/p/1I1Me
Tunesien Libyen Anti-Dschihadisten-Zaun
Hoto: Getty Images/AFP/F. Belaid

Jaridar Le Monde ta kasar Faransa ta ce dakarun Faransa na musamman da kwamandojin leken asiri hade da Amirka da Birtaniya na wani yaki cikin sirri da mayakan kungiyar IS a Libya. Jaridar ta ce shugaba Francois Hollande ne ya amince da aikin soji ba bisa doka ba a kasar ta Libya mai gwamnatoci biyu kishiyoyin juna. A wani abin da jaridar ta kira yakin Faransa na sirri a Libya, ta ce dakarun kasar na kai hare-hare kan jagororin kungiyar ta IS, a wani yunkuri na karya karfin kungiyar a Libya. Ma'aikatar tsaron Faransa ba ta ce uffa ga rahoton jaridar ta Le Monde ba, amma majiyoyi na kusa da ministar tsaro Jean-Yves Le Drian sun ce ministan ya ba da umarnin gudanar da bincike kan karya dokokin sirri na tsaron kasar kana kuma a gano inda labarin ya fito.