1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai hari a cikin masallaci a Maiduguri

Abdul-raheem HassanJuly 8, 2016

Dan kunar bakin wake ya yi sanadiyyar mutuwar mutane shida a cikin babban masallacin Damboa da ke a jihar Bornon Najeriya.

https://p.dw.com/p/1JLtX
Nigeria Anschlagsort in Kano
Hoto: DW/J.P. Scholz

Mutane shida sun mutu a wani sabon harin kunar bakin wake a wannan Jumma'a a garin Damboa dake jihar Borno a Arewa maso Gabashin Najeriya. Mai magana da yawun rundunar sojin Najeriyar Kanal Sani Usman Kuka Sheka ya sheda wa kamfanin dillacin labaru na AFP cewa "Maharin ya tada bam din da ke jikinsa ne a cikin babban masallacin Jumma'a na Damboa, inda nan take ya hallaka kansa da wasu mutane shida da ke ibada a cikin masallacin."

Kawo yanzu babu cikakkun bayanai a kan wadanda suka dau alhakin kai wannan hari, to amma a baya kungiyar Boko Haram ta sha daukar alhakin kai irin wadannan hare-hare da ke sanadiyyar rayukan al'umma a arewacin Najeriyar.