1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dangantakar Isra'ila da Gaza na muni

April 2, 2018

Alkaluman wadanda suka halaka a rikicin iyakar Gaza da Isra'ila na ranar Juma'ar da ta gabata, ya kai mutum 17, dai-dai lokacin da Falasdinawa ke jan damarar zanga-zanga.

https://p.dw.com/p/2vND1
Gazakonflikt Beerdigung
Hoto: picture-alliance/dpa/Photoshot/A. Nobani

Yawan wadanda suka mutu a rikicin iyakar Gaza da Isra'ila na ranar Juma'ar da ta gabata, ya kai mutum 17 a wannan Litinin a dai-dai kuma lokacin da Falasdinawa ke jan damarar zanga-zanga mai karfi. Majalisar Dinkin Duniya da kungiyar Tarayyar Turai sun yi kiran a gudanar da cikakken bincike kan rikicin, binciken da mahukuntan Isra'ila suka nuna ja a kai.

Daruruwan Falasdinawa ne suka ji rauni a artabu tsakaninsu da sojojin Isra'ila, rikicin da aka dauki shekaru ba a ga irinsa ba tsakanin Isra'ila da Falasdinu.

Ma'aikatar lafiyar a yankin Falasdinawa ta tabbatar da mutuwar wani matashi Bafalasdinu guda a wannan Litinin, sakamakon raunin da ya ji a rikicin.

Kungiyar Hamas ta yi kiran ci gaba da zanga-zangar da ya kai sojin Isra'ila afka masu a ranar Juma'ar da ta gabata.