1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dangantakar Masar da Hizbullah

April 28, 2010

Masar ta yanke wa mutanen 26 wadanda ta ke zargi suna alaka da Hizbullah hukucin dauri a gidan yari

https://p.dw.com/p/N8kR
Husni Mubarak da Hassan NasarullahHoto: AP

Wata kotu a ƙasar Masar ta ɗaure mutane 26 wadan da aka samu da laifin alaƙa da ƙungiyar Hizbullah, inda wasu kuwa aka ɗaure su da yunƙurin kai hari wa gwamnatin ƙasar ta Misira. Alƙalin ya yankewa 'yan wannan ƙungiyar waɗanda suka haɗa da yan ƙasar ta Masar da Sudan da Lebanon da Palsdinawa ɗauri na watanni shida izuwa ɗaurin rai da rai a gidan yari. Mutanen an kama su ne a tsakanin shekara ta 2008 da kuma 2009, inda ake zarginsu da laifin shirya kai hari a wuraren shaƙatawa na ƙasar da kuma yin liƙen asiri ma wata ƙasa ta ƙetare haɗe da samunsu da bama bamai. Shugaban ƙungiyar Hizbullah Hassan Nasarullah yace sam mutane basu da wani laifi, illa kawai ɗayan wanda aka tura domin ya taimakawa Palasɗinawa waɗawanda ke ƙarƙarme a yanken Gaza.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu