1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dubban 'yan Iraki na zanga-zanga a birnin Baghdad

Kamaluddeen SaniApril 27, 2016

Dubban 'yan kasar Iraki ne a yau suka futo kwansu da kwarkwata a kan titunan birnin Baghdad domin gudanar da wata zanga-zanga da nufin tilastawa mahukuntan kasar yin wani garambawul a majalisar zartarwar kasar.

https://p.dw.com/p/1IdFg
Irak Anhänger des schiitischen Geistlichen Moqtada al-Sadr - Protest in Bagdad
Hoto: Reuters/A. Saad

Kasar Iraki dai na fusakantar matsalolin siyasa, a yayin da Firiminisatan kasar Haider al-Abadi ke cigaba da kokarin kafa sabuwar majalisar zartarwar kasar da zata hado dukkanin bangarorin da basa ga miciji da juna.

Masu zanga-zangar dai na son ganin Shugaba Haider al-Abadi daukar kwararan matakan yin tankade da rairaya a cikin gwamnatin gami da kawo karshen cin hancin da rashawar da ya yiwa kasar katutu.

Bugu da kari a yayin da duban 'yan Irakin ke cigaba da zanga zangar, tuni 'yan majalisar dokokin Irakin suka amince da nada karin wasu da Shugaba Haider al-Abadin ya mika musu wadanda za a dana a mukaman ministocin kasar.