1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU :Nan gaba kadan ne za a janye wa Iran takunkumi

Kamaluddeen SaniJanuary 11, 2016

Kantomar manufofin Kungiyar Tarayyar Turai Federica Mogherini ta bayyana cewar kungiyar bata da wani tartibin lokaci da aka ajiye don janyewa Iran takunkumi.

https://p.dw.com/p/1HbbU
Federica Mogherini und Mohammad Javad Zarif Iran
Hoto: picture-alliance/dpa

Federica Mogherini ta yi nuni da cewar aiwatar da yarjejeniyar na tafiya kamar yadda aka tsara,kana abin karfafa gwiwa ne,na yi magana ta wayar tarho a kan batun da ministan harkokin wajen Iran Javad Zarif kwanaki kalilan da suka wuce da kuma John Kerry jiya abubuwa na tafiya dai-dai don haka muna ganin nan gaba kadan za a fara aiwatar da shirin janye kakunkumin.

Iran ta tsimma yarjejeniya ce kan makaman nulikiyar ta ne da kasashe biyar na yammacin duniya a shekarar da ta gabata a bisa sharadin musayar janye mata takunkumin da aka sanya mata wanda ya da kushe tattalin arzikinta.