1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU za ta kai Faransa kotu

September 29, 2010

Kasar Faransa za ta fiskanci shari'a, bisa matakan da ta ɗauka na korar baƙi, 'yan asalin Tarayyar Turai

https://p.dw.com/p/PQ8k
Shugaba Nicolas SarkozyHoto: picture-alliance/dpa

Hukumar Tarayyar Turai ta ɗauki matakan gabatar da ƙasar Faransa a gaban kotu, sakamakon saɓa dokar 'yancin walwala ta Tarayyar Turai, inda Faransa ta kori 'yan ƙabilar Roma dake ƙasar ta. Kwamishiniyar shari'a ta ƙungiyar Tarayyar turai wato EU, Viviane Reding ta ce Faransa ta karya doka, bayan tilastawa 'yan ƙabilar Roma kimanin dubu takwas (8000) da su fice daga ƙasarta, kana ta tasa ƙiyarsu izuwa ƙasashensu na asali wato Romaniya da Bulgariya. Wannan matakin gabatar da Faransa gaban kotu zai shafi dangantakar Faransa da EU sosai, kasancewa shugaba ƙasar Faransa Nicolas Sarkozy ya ƙeƙesa ƙasa, ya kare korar baƙin.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Yahouza Sadissou Madobi