1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU za ta kara wa Koriya ta Arewa takunkumi

Ahmed Salisu
September 7, 2017

Kungiyar Tarayyar Turai ta EU ta ce za ta kara wa Koriya ta Arewa takunkumi biyo bayan gwaje-gwajen makamai masu linzami da ka iya cin dogon zango wanda ta ke cigaba da yi.

https://p.dw.com/p/2jTiR
Nordkorea Kim Jong-Un
Hoto: Getty Images/AFP/STR

Kantomar da ke kula da harkokin wajen ta Kungiyar EU din Federica Mogherini ce ta ambata hakan a watan zantawa da ta yi da manema labarai kan takun sakar da aka cigaba da samu tsakanin Arewa da makotanta musamman ma Koriya ta Kudu kan gwaje-gwajen makamai. Mogherini ta ce nan gaba a yau za ta tattauna da ministocin harkokin wajen EU din a Estoniya kan batun Koriya ta Arewa inda ta ke cewar za ta bada shawarar a karawa Arewan takunkumin karya tattalin arziki. Kantomar ta ce duniya na fuskantar barazana sakamakon dabi'ar Pyongyang kuma ba za a barta ta yi kafar ungulu ga sha'anin tsaro da zaman lafiyar da kasashen duniya ke cin moriya ba.