1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fada ta barke a Guinee

November 15, 2010

Soojoji sun tarwatsa wasu mata da ke kokarin tayar da fitina a Conakry babban birnin kasar Guinee

https://p.dw.com/p/Q8zU
Matasa masu zanga zanga a GuineaHoto: AP

An bada rahoton cewa fada ta barke tsakanin jam'ian tsaro da da wasu daruruwan matasa a Conakry Babban birnin kasar Guinee, a dadai lokacin da ake cikin zaman jiran hukumar zabe ta kasar ta bayyana sakamakon zaben  na shugaban kasar da aka gudanar a makon jiya.

Wani babban jam'in yan sanda da ya ce sun tarwatsa matasan galibi magoya bayan tsohon Firaminista Cellou Dalein Diallo,

ya ce suna kokarin tayar da fitinan ne a wata cibiyar ta yan siyasar a sa'ilin da suka fatatakesu.Nan da wani lokaci ne dai a yau aka shirya hukumar zaben za ta bayyana dan taraka da yayi nasara a zaben shugaban kasar zagaye na biyu tsakanin Alpha Conde da Mista Diallo.

Mawallafi : Abdurahamane Hassane

Edita        : Abdullahi Tanko Bala