1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fadan Juba ya kawo asara da yawa

Usman Shehu UsmanJuly 17, 2016

Mako guda bayan fada a Juba babban birnin kasar Sudan ta Kudu har yanzu ana ci gaba da zintar gawakin da ke yashe a kusa da tankunan sojoji da aka kana.

https://p.dw.com/p/1JQPV
Südsudan Juba SPLA Rebellen
Hoto: Getty Images/AFP/S. Bol

Hakan na faruwa ne mako guda bayan kazamin fafatawa da aka yi tsakanin sojojin da ke gaba da juna bisa neman iko, a kasar da ta balle daga gwamnatin Khartum. Daruruwan mutane ne dai suka mutu a gumurzun da aka yi. A watan Disamban shekara ta 2013 ne, yaki ya barke tsakanin magoya bayan shugaba Salva Kiir da na mataimakinsa Rieck Machar. A watan Aprilun bana ne Rieck Machar ya dawo Juba domin rike mukamin mataimakin shugaban kasa, a wata yarjejeniyar jeka na yika da aka cimma, don kafa gwamnatin hadaka. A wannan Litinin ne aka cimma wata kwarya-kwaryar yarjejeniyar tsagaita wuta, to amma babu wanda ya san abinda ka iya faruwa a wannan kasar, da ta kasa samun zaman lafiya tun samun yancin kanta.