Fadan Juba ya kawo asara da yawa
July 17, 2016Talla
Hakan na faruwa ne mako guda bayan kazamin fafatawa da aka yi tsakanin sojojin da ke gaba da juna bisa neman iko, a kasar da ta balle daga gwamnatin Khartum. Daruruwan mutane ne dai suka mutu a gumurzun da aka yi. A watan Disamban shekara ta 2013 ne, yaki ya barke tsakanin magoya bayan shugaba Salva Kiir da na mataimakinsa Rieck Machar. A watan Aprilun bana ne Rieck Machar ya dawo Juba domin rike mukamin mataimakin shugaban kasa, a wata yarjejeniyar jeka na yika da aka cimma, don kafa gwamnatin hadaka. A wannan Litinin ne aka cimma wata kwarya-kwaryar yarjejeniyar tsagaita wuta, to amma babu wanda ya san abinda ka iya faruwa a wannan kasar, da ta kasa samun zaman lafiya tun samun yancin kanta.