1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa ta ce a miƙa mata 'yan ƙasarta da aka yankewa hukunci a Chadi

December 27, 2007
https://p.dw.com/p/CgfY

Hukumomin ƙasar Faransa sun bukaci a miƙa Faransawan nan shida da aka yanke musu hukunci a Chadi ga kasar ta Faransa. Wata kotu a Chadi ta yanke hukuncin ɗaurin shekaru takwas takwas a gidan yari bisa laifin yunƙurin bautad da wasu yara ƙanana,bayan an kama su da laifin satar yara 103 daga Chadi. A watan Oktoba aka tsare membobin ƙungiyar agaji ta Zoes Ark a lokacinda suke ƙoƙarin fita da yaran dukkaninsu yan shekaru ƙasa da goma zuwa turai. Iyayen yaran sun ce sun miƙa yaran nasu ne bisa imanin cewa za a sanya su makaranta ne a wani gari dake gabacin Chadi .