1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Firaministan Somalia Ghedi ya yi roko da a kai musu dauki

September 26, 2006
https://p.dw.com/p/BuiH
Firaministan Somalia Ali Mohammed Ghedi ya yi kira ga kasashen duniya da suka kai musu dauki don tinkarar barazana ta karuwar aikin ta´addanci a kasar. FM ya yi roko da a ba su taimako don hana kungiyar al-Qaida samun gindin zama a Somalia. FM Ghedi yayi wannan kira ne bayan da sojojin sa kai na kotunan Islama suka fadada ikonsu bayan sun kwace birnin Kismayo mai tashar jiragen ruwa a ranar lahadi da ta wuce. Rahotanni sun shaidar da cewa an kashe mutane 3 ciki har da wani yaro mai shekaru 13 a duniya sakamakon fadan na baya bayan nan. Kotunan Islaman wadanda suka musanta duk wata alaka da al-Qaida sun ce sun kwace birnin na Kismayo ne don hana wata rundunar kungiyar tarayyar Afirka shiga kasar. Gwamnatin wucin gadin Somalia dake da mazauni a Baidoa ta zargi ´yan Islaman da daukar sojojin sa kai daga Eritrea, Pakistan da Yemen, abin da ya karya dokokin yarjejeniyar zaman lafiyar Somalia da aka kulla a Sudan.