1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Tattalin arziki

G20: Taro kan bunkasa abinci a duniya

Zainab Mohammed Abubakar
January 22, 2017

Samar da ingantaccen abinci da yawan mutanen da ke karuwa a duniya, su ne manyan batutuwa da taron ministocin harkokin noma zai yi nazari a kai a birnin Berlin.

https://p.dw.com/p/2WCrW
Maispflanze
Hoto: picture alliance/dpa

Taron da ke gudana a birnin Berlin fadar gwamnatin Tarayyar Jamus zai hada da kwararru a bangaren noma daga kasashen kungiyar ta G20 masu bunkasar tattalin arziki. Kazalika mahalarta taron zasu jaddada bukatar alkinta ruwa da inganta harkokin noma na zamani. Taron da ke bangaren bukin "makon kare muhalli" a nan Jamus da ake kira da "Grünner Woche" na zama irinsa na farko da kungiyar kasashe masu bunkasar tattalin arzikin na G20 ke gudanarwa a wannan shekara. A wannan  Asabar din dai, kimanin mutane dubu 10 ne suka gudanar da gangami a birnin na Berlin, a wani mataki na neman a inganta sashen noma.