1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gabashin birnin Kudus babban birnin Falasdinu

Abdourahamane Hassane
December 13, 2017

Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya yi kira ga kasashen duniya da su aminci da gabashin birnin Kusdus a matsayin babban birnin Falasdinu.

https://p.dw.com/p/2pIVq
Türkei Sondergipfel der Organisation für Islamische Kooperation (OIC)
Hoto: Reuters/K. Ozer

Recep Tayyip Erdogan ya yi wannan kira ne a wajen taron kungiyar kasashe Msulmi OIC ko kuma  OCI da ke gudana a birnin Istanbul. Sai dai a halin da ke ciki  kasashe da dama na Musulmi ba sa son yin ja in ja da Amirka da kuma ma Isra'ila. Amma dai tuni da kasashen Iran da Jodan da Qatar da Libanon da kuma Sudan wadanda shugabanninsu ke halarta taron suka amsa kira na shugaban Turkiyya.