1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gaza kare fararen hula a Sudan ta Kudu

November 1, 2016

Bincike ya nuna dakarun kiyaye zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya sun gaza kan kare fararen hula a Sudan ta Kudu.

https://p.dw.com/p/2S0Hj
Südsudan Einwilligung Sationierung zusätzlicher Blauhelmsoldaten
Hoto: picture-alliance/AP Photo/J. Lynch

Wani binciken Majalisar Dinkin Duniya ya nuna cewa dakarun kiyaye zaman lafiya na majalisar da ke aikin wanzar da zaman lafiya a Sudan ta Kudu sun gaza mayar da martani bisa harin da sojojin gwamnati suka kai kan fararen hula. Binciken ya nuna an kai hari a waje mai nisan kasa da mil daya da sansanin dakarun kiyaye zaman lafiyar.

An daura alhakin haka kan rashin shiri, da rashin shugabanci na gari gami da tunanin abin da martanin zai haifar. Kasar ta Sudan ta Kudu ta fama cikin rikicin tun sabanin da ya kunno kai tsakanin Shugaba Salva Kiir da tsohon mataimakinsa Riek Machar.