1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Germanwings: Za a kai ƙara a gaban wata kotu a Amirka

Abdourahamane HassaneApril 13, 2016

Wasu daga cikin Iyalen mutanen nan,waɗanda haɗarin jirgin saman kamfanin sufirin jiragen sama na Jamus Germanwings ya rutsa da yan uwansu a shekara bara sun ce za su kai makarantar da matuƙin da ya yi karatu ƙara.

https://p.dw.com/p/1IUvm
Flughafen Hamburg
Hoto: picture-alliance/dpa/A. Heimken

Iyalen un ce za su kai makarantar da matukin jirgin Andreas Lubitz ya yi karatu inda ya samu horo daga shekara ta 2010 zuwa ta 2011 ƙara a gaban wata kotu da ke a Amirka.
Makarantar ta horas da matuƙa jirgin sama mai sunan ATCA da ke a Arizona a kudu maso yammacin Amirka.Iyalen fasinjan da suka mutu na zarginta da nuna sakaci, wajen karɓar dalibin duk kuwa da cewar a cikin takardunsa na shaida na kiwon lafiya an nuna cewar a baya ya fi fama da tabin hankali.

A cikin watan Maris na shekara bara marigayi Lubitz ya faɗi da jirgin saman na kamfanin na Germanwings da ke ɗauke da fasinja 149 a cikin tsaunikan Faransa wanda daga cikinsu babu wanda ya fita har shi.