1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Girgizar kasar mai karfi ta afka wa Kudancin Chile

Yusuf BalaSeptember 17, 2015

Wannan girgiza dai ta sanya jijjigar gine-gine a birnin Santiago da tazarar kilomita 280 daga Kudanci sannan wasu yankunan da ke a kusa da gabar teku sun shiga fargabar Tsunami.

https://p.dw.com/p/1GXhv
Chile Erdbeben
Al'ummar Chile bayan girgizar kasaHoto: Reuters/R. Garrido

Girgizar kasa mai karfin maki 8.3 a ma'aunin Richter da ta afkawa gabar teku a Chile a daren jiya Laraba ta yi sanadin halaka mutane biyar da tilasta kimanin miliyan daya kauracewa muhallansu.

Wannan girgiza dai ta sanya jijjigar gine-gine a birnin Santiago da tazarar kilomita 280 daga Kudanci sannan wasu yankunan da ke a kusa da gabar teku sun shiga fargaba ta yiwuwar samun Tsunami.

Tuni dai shugaba Michelle Bachelet ta bayyana shirinta na ziyartar wurin da lamarin ya afku , wanda ke zama mafi muni a wannan kasa tun bayan wanda ta gani a shekarar 2010.

Masana dai sun bayyana cewa a zauna cikin shiri a yankunan da ke a Amirka ta Kudu da Hawaii da California duk da cewa torokon ruwa da ake tsammani zai dan lafa. An dai ga mutane a kasar ta Chile a kan tituna cikin rudani da firgici.