1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gobara ta halaka mutane da dama a Indiya

Suleiman BabayoApril 10, 2016

Gobarar ta tashi a wajen bauta na mabiya addinin Hindu da ke yankin kudancin Indiya inda mutane kimanin 80 suka halaka wasu fiye da 200 suka samu raunuka.

https://p.dw.com/p/1ISi5
Indien Kollam Tempel Feuer
Hoto: Reuters/ANI

Kusan mutane 80 sun hallaka yayin da wasu fiye da 200 suka samu raunuka sakamakon gobarar da ta tashi a wajen bauta na mabiya addinin Hindu da ke Jihar Kerala a yankin kudancin kasar Indiya. Wani babban jami'in jihar ya ce lamarin na wannan Lahadi ya faru lokacin da aka samu fashewa. Abin wasa da wuta ya haddasa fashewar lokaci biki na mabiya addnin Hindu.

Akwai yiwuwar samun karin yawan wadanda suka halaka sakamakon gobarar ta Indiya.