1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Guterres ya yi rantsuwar maye gurbin Ban Ki-moon

Yusuf Bala Nayaya
December 12, 2016

Antonio Guterres ya zama Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya inda ya ke zama na tara a layi.

https://p.dw.com/p/2UAU1
UN Generalversammlung - Antonio Guterres, Vereidigung als Generalsekretär in New York
Hoto: picture-alliance/dpa/J. Lane

Tsohon Firaministan Potugal Antonio Guterres  ya yi rantsuwar kama aiki a ranar Litinin din nan a matsayin Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya inda ya ke zama na tara a layi, ya rattaba hannu kan wannan aiki gaban babban taron mai mambobi 193.

Guterres  mai shekaru 67 zai maye gurbin Ban Ki-moon mai shekaru 72 dan asalin Koriya ta Kudu daga ranar daya ga watan Janairu mai zuwa, abin da zai kawo karshen wa'adi biyu na shekara biyar-biyar da  Ban Ki-moon ya yi.

Guterres dai baya ga firaminista tsakanin shekarar 1995 zuwa 2002 ya rike kwamishina na Majalisar Dinmkin Duniyar kan 'yan gudun hijira tun daga shekarar 2005 zuwa 2015.