1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnatin Jamus ta koma da 'yan Afghanistan 125 gida

Mohammad Nasiru AwalFebruary 24, 2016

A makonnin bayan nan dai yawan 'yan gudun hijira daga Afghanistan da ke shigowa Jamus ya karu.

https://p.dw.com/p/1I1Dp
Afghanistan Flüchtlinge Rückkehr in ihrem Heimat
Hoto: DW

A wani abin da ke zama wata matsalar 'yan gudun hijira da take fuskanta, a karon farko Jamus ta koma da 'yan Afghanistan 125 gida. Tuni dai jirgin saman da ya kwashi 'yan gudun hijirarya isa birnin Kabul, inji ma'aikatar cikin gidan Jamus da ke birnin Berlin, wadda ta kara da cewa 'yan Afghanistan din sun koma gida ne don radin kai bayan an hana su takardun izinin zama a Jamus. Wata yarjejeniya da gwamnatin tarayyar Jamus ta kulla da mahukuntan Afghanistan ta tanadi mayar da masu neman mafakar siyasa da aka yi watsi da bukatunsu, gida. Jamus dai na mai ra'ayin cewa a Afghanistan akwai wurare masu tsaro da kwanciyar hankali da 'yan kasar wadanda suka tsere daga ta'asar Taliban, za su iya zama ciki. A makonnin bayan nan yawan 'yan gudun hijira daga Afghanistan ya karu.