1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnatin Somalia ta yi fatan girke sojojin kiyaye zaman lafiya a kasar

January 1, 2007
https://p.dw.com/p/BuVp

Bayan an fatattaki sojojin sa kai na kawance kungiyar kotunan Islama, yanzu gwamnatin wucin gadi ta Somalia na fatan girke dakarun kiyaye zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afirka AU a kasar. FM Mohammed Ali Gedi ya fada a birnin Mogadishu cewa girke dakarun AU zai taimaka wajen samar da zaman lafiya da daidaita al´amura a cikin kasar sa. Tare da taimakon sojojin Ethiopia a yau dakarun gwamnati suka karbi ikon kudancin kasar wanda ya kasance yanki na karshe a hannun mayakan na kotunan Islama. Bayan nasarar da suka samu, FM Gedi ya ce za´a ci-gaba da fatattakan ´yan Islama.