1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jirgin saman kasar Senegal ya yi hadari

Lateefa Mustahpa JaafarSeptember 6, 2015

Wani jirgin sama na daukar marasa lafiya ya yi hadari a kan hanyarsa ta isa Dakar dauke da mutane bakwai ciki kuwa har da wani mara lafiya dan kasar Faransa.

https://p.dw.com/p/1GRsI
Symbolbild Luftbrücke Westafrika Transall
Hoto: picture-alliance/dpa/Bernd Wüstneck

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Sanegal ta sanar da cewa jirgin mallakar wani kamfani mai zaman kansa na kasar ya taso ne daga Ouagadougou na kasar Burkina Faso kuma ya bace an daina jin duriyarsa tun a yammacin wannan Asabar da misalin karfe bakwai agogon GMT a yayin da yake kimanin nisan kilomita 111 da yammacin Dakar babban birnin kasar ta Senegal. Tuni dai dakarun sojojin sama na kasar ta Senegal suka isa inda ake kyautata zaton jirgin ya fadi domin gudanar da bincike.