1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hamas na tunanin neman mafita

February 9, 2006
https://p.dw.com/p/Bv8l

Kungiyyar Hamas ta masu kishin Islama, tace zata bukaci tallafi na batutuwa da suka jibanci siyasa da kudi daga kasashen larabawa da kuma wasu kasashen Musulmai.

A cewar daya daga cikin shugabannin kungiyyar, wato Khaled Meshal, sun kudiri aniyar yin hakan ne don yin kandagarki a game da kurarin da kasashen yamma keyi na tsayar da tallafin raya kasa da suke bawa yankin.

A dai jiya ne ministar harkokin wajen Amurka CR tace kasashen yamma zasu tsayar da tallafin da suke bawa yankin, matukar basu amince da kasancewar Israela a matsayin kasa ba.

Kafin dai wannan bayani, na CR, a can baya Ministan harkokin wajen Israela, ya bukaci kasashen duniya dasu kauracewa yankin na Palasdinawa matukar kungiyyar ta Hamas ta kafa gwamnati.