1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hamas ta mayar da wuraren Fatah dake Gaza ƙarƙahin ikon ta

June 14, 2007
https://p.dw.com/p/BuIx

A dangane da rikici mai kama da yakin basasa da ke kara yin muni tsakanin kungiyoyin Falasdinawa da ba sa ga maciji da juna, shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas da FM Isma´il Haniya sun yi kira da a kawo karshen tashe tashen hankukla a Zirin Gaza. Sun yi kira ga magoya bayansu da su daina fada nan take. Da farko kungiyar Hamas ta mayar da wurare da dama a Zirin na Gaza karkashin ikonta bayan ta mamaye kusan dukkan hedkwatocin jami´an tsaro dake da alaka da Fatah. Sojojin sa kai na Hamas sun mamaye birnin Khan Yunis sannan suna ci-gaba da dannawa zuwa Rafah dake kudancin yankin. Akalla mutane 60 aka kashe a fadan da aka kwashe kwanaki ana yi a yankin na Falasdinawa.