1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hamas ta yi watsi da bukatar girke dakarun duniya a Zirin Gaza

June 30, 2007
https://p.dw.com/p/BuHX
Kungiyar Hamas ta masu kishin Islama ta yi watsi da bukatar da shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas ya nuna dangane da tura dakarun kasa da kasa a Zirin Gaza. Hamas mai mulki a Zirin na Gaza ta ce za´a kaiwa wadannan dakaru hari idan aka girke su a yankin. Bayan ganawar da ya yi da sabon shugaban Faransa Nikolas Sarkozy a birnin Paris, Abbas ya nuna cewa girke wata rundunar kasa da kasa a Zirin Gaza ka iya tabbatar da kwanciyar hankali a yankin tare da gudanar da zabe na gama gari.