1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-hare a birnin Dhaka na Banlgadesh

Abdourahamane HassaneJuly 1, 2016

An ba da rahoton cewar wasu mutane dauke da makamai sun kai hari a kan wani otel wanda baki yan kasashen waje ke sauka a Dhaka babban birnin kasar ta Bangladesh.

https://p.dw.com/p/1JHkb
Bangladesch Anschlag Schießerei in Dhaka
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Ya zuwa yanzu dai babu wani karin bayyani da aka samu dangane da wannan al'amari sai dai wasu shaidu sun ce sun ji karar bindigogi a otel din da ke a wata unguwar da ke da jami'an diplomasiya na kasashen waje da dama a birnin na Dhaka.

Ofishin jakadacin Amirka a bisa shafinsa na Twitter ya ce harin ya hada har da yin gakuwa da mutane.