1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hari kan jami'an tsaro a kasar Masar

Lateefa Mustapha Ja'afarJuly 19, 2015

'Yan bindiga daga kungiyar tsagerun yankin Sinai na kasar Masar sun kai wani hari a shingayen duba ababen hawa guda biyu a kasar tare da hallaka wasu sojoji.

https://p.dw.com/p/1G19k
Hare-haren tsageru a Sinai
Hare-haren tsageru a SinaiHoto: picture-alliance/AP Photo/A. A. Schalit

Kamfanin dillancin labaran kasar ta Masar MENA ya ruwaito cewar harin da suka kai a kusa da garin Sheikh Zuweid ya haifar da musayar wuta tsakanin tsagerun da kuma jami'an tsaron kasar ta Masar inda akalla sojoji biyar suka rasa rayukansu.

Ko da a ranar daya ga wannan wata na Yuli da muke ciki ma dai kungiyar tsagerun yankin na Sinai da ke da alaka da kungiyar 'yan ta'addan IS ta kai hari a wadannan shingayen duba ababen hawan, kana a farkon mako mai karewa ma sai da kungiyar ta kai wani hari a kan rundunar sojojin ruwa ta Masar din.