1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

harin ƙunar baƙin wake a Kamaru

Abdourahamane HassaneNovember 29, 2015

Aƙalla mutane guda biyar suka mutu a cikin wasu tagwayen hare-hare na kunar baƙin wake a Yankin arewa mai nisa na Kamaru.

https://p.dw.com/p/1HEBY
Symbolbild Gewalt in Nigeria
Hoto: AMINU ABUBAKAR/AFP/Getty Images

Wasu mata ne guda biyu suka kai hare-haren a garin Dabanga da ke a yankin Arewa mai nisa na ƙasar.Gwamnan Yankin na arewa mai nisa Midjinyawa Bakary ya sanar da cewar ɗaya daga cikin matan,ta tayar da bam ɗin ne a cikin wani gidan iyalai, yayin da ɗaya ta tarwtsa kanta a cikin wani shago.

Ya zuwa yanzu ba a da masaniya dangane da waɗanda ke da alhakin kai harin. Sai dai ana kyautata zaton cewar Ƙungiyar Boko Haram ce ke da alhaki, saboda ta yi kaurin suna a wannan fanni.