1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin bam ya kashe mutane 5 a Maiduguri

Ramatu Garba Baba
December 12, 2017

 A Najeriya wasu mutum biyar sun mutu bayan fashewar da aka samu a sansanin 'yan gudun hijra da ke kusa da garin Gwoza a jahar Borno a yammancin jiya Litinin a daidai lokacin da likitocin MSF ke tsakiyar aikinsu.

https://p.dw.com/p/2pEVQ
Nigeria Ärzte ohne Grenzen in Borno
Hoto: MSF/C. Magone

A cewar kanar Oynema Nwachukwu kakakin rundunar soji da ke a birnin Maiduguri, harin ya auku ne a yayin da jami'an likitocin kungiyar agaji ta MSF ke tsakiyar aikin kulawa da al'ummar da ke rayuwa a sansanin.Da farko acewar jami'an kungiyar an yi tunanin harin kunar bakin wake aka kai, amman bayan bincike an gano ba haka batun ya ke ba, kawo yanzu ba a tabbatar da ko dasa abin fashewar aka yi ba a cikin sansanin. Akwai wadanda ake bai wa kulawa a asibiti a sanadiyar raunin da suka samu daga fashewar.

Hakazalika an tabbatar da mutuwar wasu sojoji biyu a ranar Lahadin da ta gabata bayan da motar da suke tafe a ciki ta bi ta kan wasu abubuwan fashewa da ake zargin mayakan kungiyar Boko Haram da danawa a hanyar Damboa na birnin Maidugurin jahar Borno a arewa maso gabashin Najeriya mai fama da ayyukan ta'addanci.