1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin kunar bakin wake a Kamaru

Abdourahamane Hassane
July 1, 2017

An ba da rahoton cewar wasu mata 'yan kunar bakin wake guda hudu sun tarwatsa kan su da bama-bamai da ke a jikin su a garin Mora da ke yankin arewa mai nisa na Kamaru.

https://p.dw.com/p/2flxF
Kamerun Anschlag in Maroua
Hoto: Getty Images/AFP/Stringer

Wata majiyar rundunar sojojin kasar ta Kamaru ta ce matan guda hudu da ke dauke da jigidar abubuwan da ke fashewa sun yi yunkurin shiga garin na Mora a lokacin da 'yan banga suka gano su, suka tayar da bama-baman da ke a jinkin su daf da shigowar garin. Garin na Mora da ke a arewacin Kamarun a nan ne aka jibge dakarun rundunar hadin gwiwa na kasa da kasa FMM da ke yaki da kungiyar Boko Haram.